Ticker

6/recent/ticker-posts

Cape Town: Yadda Zikirin Musulunci ke daƙile rikicin ƴan daba da shaye-shaye a Afirka Ta Kudu


 

Wata tawagar malaman addinin Musulunci a Afirka Ta Kudu ta shafe shekara uku tana wani ƙoƙari na yaɗa zaman lafiya a garin Manenberg da sauran yankunan birnin Cape Town da ake fama da matsalar ƴan daba da masu shaye-shayen miyagun ƙwayoyi.

Mai ɗaukar hoto Shiraaz Mohamed ya bi tawagar yayin wata ziyarar mako-mako da take kaiwa: 


 

Yawanci da yammacin ranakun Alhamis malaman na zuwa yankunan da 'ƴan daban suke a Cape Town don gudanar da zikiri.

A taron zikirin ana yawan ambaton Allah da yi wa Annabi salati.

Post a Comment

0 Comments